Hausa
Surah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) - Aya count 78
الرَّحْمَٰنُ 
( 1 ) 
(Allah) Mai rahama.
عَلَّمَ الْقُرْآنَ 
( 2 ) 
Yã sanar da Alƙur'ani.
خَلَقَ الْإِنسَانَ 
( 3 ) 
Yã halitta mutum.
عَلَّمَهُ الْبَيَانَ 
( 4 ) 
Yã sanar da shi bayãni (magana).
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ 
( 5 ) 
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ 
( 6 ) 
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ 
( 7 ) 
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ 
( 8 ) 
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ 
( 9 ) 
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ 
( 10 ) 
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ 
( 11 ) 
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ 
( 12 ) 
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 13 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ 
( 14 ) 
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ 
( 15 ) 
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 16 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ 
( 17 ) 
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 18 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ 
( 19 ) 
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ 
( 20 ) 
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 21 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ 
( 22 ) 
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 23 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ 
( 24 ) 
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 25 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ 
( 26 ) 
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ 
( 27 ) 
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 28 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ 
( 29 ) 
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 30 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ 
( 31 ) 
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 32 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ 
( 33 ) 
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 34 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ 
( 35 ) 
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 36 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ 
( 37 ) 
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 38 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ 
( 39 ) 
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 40 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ 
( 41 ) 
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 42 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ 
( 43 ) 
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ 
( 44 ) 
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 45 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ 
( 46 ) 
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 47 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
ذَوَاتَا أَفْنَانٍ 
( 48 ) 
Mãsu rassan itãce.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 49 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ 
( 50 ) 
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 51 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ 
( 52 ) 
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 53 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ 
( 54 ) 
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 55 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ 
( 56 ) 
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 57 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ 
( 58 ) 
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 59 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ 
( 60 ) 
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 61 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ 
( 62 ) 
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 63 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُدْهَامَّتَانِ 
( 64 ) 
Mãsu duhun inuwa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 65 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ 
( 66 ) 
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 67 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ 
( 68 ) 
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 69 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ 
( 70 ) 
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 71 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ 
( 72 ) 
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 73 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ 
( 74 ) 
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 75 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ 
( 76 ) 
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ 
( 77 ) 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ 
( 78 ) 
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.