Hausa
Surah Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya count 30
وَالْفَجْرِ 
( 1 ) 
Inã rantsuwa da alfijiri.
وَلَيَالٍ عَشْرٍ 
( 2 ) 
Da darũruwa gõma.
وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ 
( 3 ) 
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ 
( 4 ) 
Da dare idan yana shũɗewa.
هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ 
( 5 ) 
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ 
( 6 ) 
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ 
( 7 ) 
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ 
( 8 ) 
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ 
( 9 ) 
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ 
( 10 ) 
Da Fir'auna mai turãku.
الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ 
( 11 ) 
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ 
( 12 ) 
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ 
( 13 ) 
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ 
( 14 ) 
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ 
( 15 ) 
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ 
( 16 ) 
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ 
( 17 ) 
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ 
( 18 ) 
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا 
( 19 ) 
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا 
( 20 ) 
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا 
( 21 ) 
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا 
( 22 ) 
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ 
( 23 ) 
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي 
( 24 ) 
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ 
( 25 ) 
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ 
( 26 ) 
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ 
( 27 ) 
Yã kai rai mai natsuwa!
ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً 
( 28 ) 
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
فَادْخُلِي فِي عِبَادِي 
( 29 ) 
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
وَادْخُلِي جَنَّتِي 
( 30 ) 
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).