Hausa
Surah Abasa ( He frowned ) - Aya count 42
عَبَسَ وَتَوَلَّىٰ 
( 1 ) 
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
أَن جَاءَهُ الْأَعْمَىٰ 
( 2 ) 
Sabõda makãho yã je masa.
وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىٰ 
( 3 ) 
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ الذِّكْرَىٰ 
( 4 ) 
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىٰ 
( 5 ) 
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
فَأَنتَ لَهُ تَصَدَّىٰ 
( 6 ) 
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ 
( 7 ) 
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
وَأَمَّا مَن جَاءَكَ يَسْعَىٰ 
( 8 ) 
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
وَهُوَ يَخْشَىٰ 
( 9 ) 
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ 
( 10 ) 
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ 
( 11 ) 
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
فَمَن شَاءَ ذَكَرَهُ 
( 12 ) 
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
فِي صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ 
( 13 ) 
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍ 
( 14 ) 
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
بِأَيْدِي سَفَرَةٍ 
( 15 ) 
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
كِرَامٍ بَرَرَةٍ 
( 16 ) 
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
قُتِلَ الْإِنسَانُ مَا أَكْفَرَهُ 
( 17 ) 
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ 
( 18 ) 
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ 
( 19 ) 
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ 
( 20 ) 
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ 
( 21 ) 
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنشَرَهُ 
( 22 ) 
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ 
( 23 ) 
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ إِلَىٰ طَعَامِهِ 
( 24 ) 
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا 
( 25 ) 
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا 
( 26 ) 
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
فَأَنبَتْنَا فِيهَا حَبًّا 
( 27 ) 
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
وَعِنَبًا وَقَضْبًا 
( 28 ) 
Da inabi da ciyãwa.
وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا 
( 29 ) 
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
وَحَدَائِقَ غُلْبًا 
( 30 ) 
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
وَفَاكِهَةً وَأَبًّا 
( 31 ) 
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
مَّتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ 
( 32 ) 
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ 
( 33 ) 
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ 
( 34 ) 
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ 
( 35 ) 
Da uwarsa da ubansa.
وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ 
( 36 ) 
Da mãtarsa da ɗiyansa.
لِكُلِّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ 
( 37 ) 
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ 
( 38 ) 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ 
( 39 ) 
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ 
( 40 ) 
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ 
( 41 ) 
Baƙi zai rufe su.
أُولَٰئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ 
( 42 ) 
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).