Select reciter
Hausa
Surah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) - Aya count 11
وَالضُّحَىٰ 
( 1 ) 
Inã rantsuwa da hantsi.
وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ 
( 2 ) 
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ 
( 3 ) 
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَىٰ 
( 4 ) 
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰ 
( 5 ) 
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَىٰ 
( 6 ) 
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَىٰ 
( 7 ) 
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَىٰ 
( 8 ) 
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ 
( 9 ) 
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ 
( 10 ) 
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ 
( 11 ) 
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).